Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Akwai yiwuwar samun ambaliyar ruwa a wannan shekarar – NIHSA

Published

on

Ma’aikatar albarkantun ruwa ta Najeriya ta yi hasashen samun ambaliyar ruwa a wannan shekarar ta 2021.

Shugaban hukumar NIHSA mai kula da harkokin ruwa da kuma muhalli, Injiniya Nze Clement Onyeaso, ne ya tabbatar da haka yayin wata zantawa da manema labarai a Abuja.

Clement, ya ce a cikin rahoton hasashen da hukumar ta yi a baya-bayan nan, jihohin Kaduna da Lagos da Borno da Nasarawa ne aka samu ambaliyar sakamakon mamakon ruwan sama.

Sauran jihohin sun hadar da Anambra da Kwara da Rivers da Enugu da Abia sai kuma jihar Ondo.

Nze, ya gargadi jihohin da ke kusa da kogunan Niger da kuma Benue da su zama cikin shiri don akwai yiwuwar samun ambaliya nan gaba kadan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!