Connect with us

Labarai

Amnesty International ta bukaci a  kawo ƙarshen ayyukan ’yan ta’adda a Jihar Zamfara

Published

on

Kungiyar Kare Haƙƙin Dan Adam,  ta Amnesty International ta bukaci da a  kawo ƙarshen ayyukan ’yan ta’adda a Jihar Zamfara,  da ta ce  rashin tsaro  ya janyo asarar daruruwan rayuka tun daga shekarar 2012 zuwa yanzu.

 

Ta cikin sanarwar da kungiyar ta fitar, a Daren jiya Asabar Amnesty ta ce hare-haren da ake kai wa al’umma sun jefa kauyuka da dama cikin halin kunci.

 

Sanarwar ta ce mazauna kauyuka kan samu gargadi kafin kai hari, ciki har da kiran waya da ake bukatar su biya kudade ko su fuskanci kisa ko garkuwa, da  maharan kan kai hari domin sace ’yan mata da dabbobi.

 

Kungiyar  ta kuma ce daruruwan kauyuka a kananan hukumomi 13 daga cikin 14 na jihar sun zama kufai bayan hare-haren, lamarin da ya sa mutane da dama suka rasa muhallan su.

 

Amnesty, ta bukaci hukumomin ƙasar nan su dauki matakan gaggawa domin kare rayukan jama’a tare da gurfanar da wadan da ake zargi a gaban kotu bisa ka’ida, don girbar abinda suka shuka.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!