Labarai
Amnesty ta zargi gwamnatin Tinubu da gaza kare rayukan yan Najeriya

Kungiyar kare hakkin Dan-adam ta Amnesty International, ta zargi gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da gaza kare rayukan ‘yan Najeriya.
Wsannan zargi dai na zuwa ne bayan da rahotonni suka bayyana cewa ‘yan bindiga sun kashe fiye da mutane ashirin a wani kauye da ake hakar ma’adinai a jihar Zamfara.
Wata sanarwa ta Daraktan kungiyar ta Amnesty International a Najeriya, Malam Isa Sanusi, ya fitar ta ce, akalla mutane hamsin da hudu aka kashe a hare-hare daban-daban a ‘yan kwnakin nan.
A makonnin baya-bayan nan ne ‘yan bindiga suka rika kai hare-hare tare da kashe mutane da kona gidaje da amfanin gona a jihohin Benue da Plateau.
You must be logged in to post a comment Login