Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

An Tashi Lafiya

An fara rushe shagunan sayar da magunguna marasa inganci a Jihar Adamawa

Published

on

Hukumar kula da sha’anin sarrafa magunguna PCN, reshen jihar Adamawa ta gudanar da wani bincike a ƙananan hukomi, kan waɗanda suka karya ƙaidojin hukumar ta hanyar rufe shagunan sayar da magunguna a Jihar.

Hakan ya biyo bayan wani sumame da jami’an hukumar suka fara, na tantance masu sayar da magunguna tare da ingancin su.

Emmanuel Egwu, mataimakin darakten hukumar kuma jami’in dake kula da jihar kan fannin sarrafa magunguna ya bayyanawa Freedom Radio cewa bayan an bawa mutum damar sayar da magani akwai buƙatar a rinƙa bibiyar al’amuran sa domin ganin abinda ya keyi.

Ya kuma ƙara da cewa “mun rufe shagunan waɗanda ake tuhuma da aikata laifuka, za kuma mu gurfanar da wasun su a gaban shari’a, domin babu wanda aka bawa damar sayar da magunguna ba tare da takardar shaida ba. Aikata hakan, laifi ne da ka iya jawo aci taron naira dubu dari biyar da kuma zaman yari har na tsawon shekaru biyu.”

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!