Ƙetare
An gaza cimma matsaya a sulhun Amurka da Iran

Tawagar manyan jamai’an Iran da Amurka sun kammala zagayen farko na zaman tattaunawar sulhu ta sa’o’i biyu a birnin Islamabad na kasar Pakistan.
Ba a sanar da matsayar zaman ba, amma wakilin BBC ya ce amincewar bangarorin biyu su yi ganawar kai tsaye alama ce ta nasara.
Kafar yaɗa labaran Iran ta ce za a ƙara wata tattaunawar a ƙarshen mako.
Wakilan Amurka ba su ce komai ba game da zaman tattaunawar sulhun.
Ɓangarorin biyu na zargin juna da karya yarjejejniyar tsagaita wuta.
Ya yinda suke neman matsaya game da batutuwa da dama da suka haɗa da wucewa ta mashigar Hormuz da janyewa Iran takunkumai da tabbatar da tsagaita wuta a Lebanon da kuma makomar shirin nukiliyar Tehran.
You must be logged in to post a comment Login