Labarai
An kama dan shekara 23 ya hadiye kullin tabar iblis guda 59
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/05/unnamed-3.jpg)
Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta kama wani mutum mai suna Okoguale Douglas a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja dauke da tabar iblis da nauyinsa ya kai gram 781.2.
A cewar NDLEA mutumin mai shekaru 23 ya hadiye tabar iblis din ne kulli 59 a cikinsa, a kokarinsa na safararta zuwa birnin Milan da ke kasar Italiya.
Hukumar ta NDLEA ta kuma ce da zaran ta kammala bincike za a gurfanar da shi gaban kotu.
You must be logged in to post a comment Login