Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

An kama wasu yan kunar bakin wake a kauyen Mushemiri a jihar Borno

Published

on

Sojojin da ke aiki a rundunar Operetion Lafiya Dole sunkama ‘yan kunnar bakin wake mata su 2 a kauyen Mushemiri dake karamar hukumar Konduga a jihar Borno.

Wannan na kunshe cikin sanarwar da rundunar sojan kasar na ta buga a shafin ta na Twitter cewa, matan da ake zargin ‘yan kunnar bakin wake ne, suna yunkurin kai hari tare da tada bom a bataliya ta 222 na rundunar sojan kasar nan dake yankin na Konduga a daren jiya Laraba.

Haka zalika a cewar sanarwar jami’an rundunar Operation Lafiya Dole sun gano cewa matan sun makale bom din a jikin su, a yayin da suke kokarin tada shi, amma jami’an suka kama su.

Sojojin sun kama su ne a dai-dai lokacin da suke binciken ababan hawa, yayin da ‘yan kunnar bakin waken suke yunkurin kai harin da misalin karfe 9 da rabe na daren jiya Laraba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!