Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar kula da kamfanoni sadarwa ta ce ta gano yadda ake cirewa kwastamomi kudade babu gaira babu dalili

Published

on

Hukumar dake kula da kamfanonin sadarwa ta kasa NCC ta sanar da cewa, ta gano yadda kamfanonin sadarwa ke cirewa kwastomomi kudade a layukan su na wayoyi babu-gaira-babu-sabar.

Hukumar ta NCC ta sanar da hakan ne a cikin shafin ta na Internet cewa, nan bada jimawa ba ne, zata baiwa kamfanonin sadarwar umarnin mai da kudaden da ta cire na kwastamomi ba tare da sahalewar su ba.

Haka zalika hukumar dake kula da sadarwa ta kasa ta ce, ta gano hakan ne, bayan da ta karbe korafe-korafen jama’a kan ana cire musu kudaden idan sun sanya kudi cikin layukan su, yayin da hukumar ta kaddamar da bincike kan batun. Sashin dake bibiyar ayyuka da bin dokoki na hukumar ta NCC ya bayyana cewar, hukumar ta aike da ayarin masu bincike don faiyace batun, bayan hakan ne sai hukumar ta bayar da layukan waya don tuntubar ta

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!