Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

An kasa cimma matsaya tsakanin gwamnatin tarayya da kungiyar malamai kwalejojin fasaha

Published

on

Gwamnatin tarayya da kungiyar malaman kwalejojin fasaha ta kasa ASUP sun kasa cimma matsaya a taron da suka gudanar a jiya domin lalubo bakin zaren matsalar su da suka ce gwamnati ta ki kula da ita.

Gwamanti da kungiyar ta ASUP sun ki amincewa da bukatun juna, inda kowa ya kafe akan bakan sa ya yin zaman na jiya, lamarin da ya janyo aka dage zaman har zuwa watan janairu mai kamawa 

Yayin zaman dai ministan Ilimi Malam Adamu Adamu ne ya wakilici gwamnatin tarayya inda kuma shugaban kungiyar ta ASUP Usman Dutse ya jagoranci kungiyar.

Da yake jawabi jin kadan bayan kammala zaman ministan ilimi Malam Adamu Adamu ya ce duka bagarorin biyu sun tashi ba tare da cimma wata matsaya ta azo a gani ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!