Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar INEC ta ce tana aiki ka’in da-na’in wajen inganta zaben badi

Published

on

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta ce, tana aikika’in-da-na-in wajen gudanar da shirye-shiryen babban zaben badi ingantacce,karbabbe kuma sahihi.

Shugaban hukumar zabe ta kasa INEC ne ya bayyana hakan a babban taron masu rike da masarautun gargajiya karo na 5 mai taken’’ Yawan fama da rashin tsaro a cikin shekarar zabe’’ da aka yi a jiya Laraba a jihar Kaduna.

Farfesa Mahamod Yakubu ya ce ‘yan siyasar kasar nan basa yin dumokuradiyya a aikace kuma sune ummul-aba-isin wajen kawo tarnaki kan rashin cigaba a harkokin dumokuradiyya a Najeriya, ganin yadda suke sauya sheka daga wannan jam’iyyar zuwa wata.

Haka zalika shugaban hukumar zaben INEC yace hukumar ba zata yi kasa a gwiwa ba wajen cigaba da gudanar da shirye-shiryen tunkarar babban zaben na badi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!