Labarai
An kawo Rukuni na biyu na ƴan Najeriya 705 da ke gudun hijira a Kamaru

Rukuni na biyu na ’yan kasar nan 705 da ke gudun hijira a ƙasar Kamaru sun dawo gida, inda suka isa garin Banki a Karamar Hukumar Bama ta Jihar Borno.
Wannan na cikin sanarwar da Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Borno, Dauda Iliya, ya fitar.
Ya ce an dawo da ’yan gudun hijirar ne daga birnin Maroua na Jamhuriyar Kamaru a jiya Alhamis.
A cewarsa, dawowar na cikin shirin ci gaba na mayar da ’yan Najeriya da rikicin tsaro ya tilasta musu barin muhallansu, tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da tallafa musu wajen sake zaunar da su su ci gaba da rayuwa.
You must be logged in to post a comment Login