Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An nemi Kotu ta hana ɗaukar hoton Ɗan Chinan da ake zargi da kisan Ummita

Published

on

Lauyan da ke kare Ɗan Chinan nan Mista Geng Quanrong, Barista Muhammad Balarabe Ɗan’azumi ya nemi Kotu ta hana ɗaukar hoton wanda yake karewa.

Ya ce, hakan tozartawa ce ga wanda ake zargi.

Sai dai mai shari’a bai ce komai ba kan wannan buƙata.

Wannan dai ya biyo bayan da lauyan Gwamnati Barista Musa Abdullahi Lawan ya nemi Kotu ta hana a riƙa ɗaukar hoton wanda yake yiwa Ɗan Chinan fassara.

Lauyan ya ce, ɗaukar hoton nasa tamkar keta mutunci ne, domin ba zarginsa ake ba, hassalima aro shi aka yi daga ofishin jakadancin ƙasar China.

Mai shari’a Sanusi Ma’aji ya amince da buƙatar lauyan Gwamnati inda ya hana sake ɗaukar hoton wanda yake fassarar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!