Connect with us

Labarai

An sace mutane 2000 tare da kashe 1500 a watanni 4 farkon 2025-NHRC

Published

on

 

Hukumar kare haƙƙin Bil-adama ta kasa  NHRC, ta ce tsakanin watan Janairun shekarar da ta gabata  zuwa Afrilun  wannan shekarar da muke ciki an sami aukuwar sace-sacen jama’a kusan 2000, ya yin da kuma aka  halaka wasu kusan 1, 500 a sassan kasar.

Ta cikin rahoton da hukumar ta fitar ta ce  an sace sama mutum 1,712 tare da kashe mutum 1, 463 a wurare daban-daban a fadin kasar nan, daga watan Janairu shekarar da ta gabata zuwa  watan Afrilun bana  lamarin ya nuna karuwar ayyukan ta’addanci musamman yankin Arewacin kasar nan.

Kwamared Kamal Adam shi ne sakataren kare hakkin Bil’adama ta kasa reshen Jihar Kano ya tabbatar da alkaluman rahotan a tattaunawarsa da Freedom Radio.

Manjo Muhammad Lawal Yaqub ,Mai ritaya Masani ne kuma mai sharhi kan lamuran tsaro a kasar nan ya ce Lokaci ya yi da za a fara samo tushen dalilan ci gaba da Afkuwar hakan.

A cewar Kwamred Bello Basi Fagge, rahoton  bai zo da mamaki ba ganin yadda matsalar tsaro ta zama wata babbar Sana’a ga wasu marasa aikin yi a kasar nan.             

Matsalar sace sacen mutanen de ta fi kamari a yankin arewacin kasar nan musamman ma yankin arewa maso Yamma, a jihohin Katsina , Kaduna , Zamfara , Sokoto da Kebbi , sai na ‘yan tada kayar baya a Arewa maso Gabas ,daga Adamawa zuwa Yobe da Borno.

Kalubalen da al’umma ke ci gaba da kiraye-kiraye ga hukumomi da su dauki matakin dakile  matsalar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!