Labaran Wasanni
An sallami Pele daga Asibiti
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/10/b216e5650f7b3ff3bde993cc56c9a86aa2ab0648.jpg)
Tsohon dan wasan kasar Brazil Pele ya koma gida bayan da aka sallameshi daga asibiti sakamakon jinya da ya sha.
Mai shekaru 80 ya kasance a bangaren masu kulawa ta musamman wato ICU tun a ranar 4 ga watan Satumbar daya gabata.
Mahukuntan asibitin ne dai suka sanar da sallamar Pele a wani rubutu da suka wallafa a shafin Internet a ranar Juma’a 01 ga watan Oktobar 2021.
Pele dan kasar Brazil wanda ya lashe gasar cin kofin Duniya har sau uku a shekarun 1958, 1962 da kuma 1970.
Kuma ya zama dan wasan guda da yafi kowa zura kwallo a tarihin kasar da yawan kwallaye 77 a wasanni 92 da ya buga.
You must be logged in to post a comment Login