Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An yiwa ‘yan wasan Adamawa United Fashi

Published

on

An yiwa ‘Yan wasan tawagar Adamawa United da mukarraban su fashi da makami a hanyar Benin zuwa Ore, cikin daren Jumma’a.

‘Yan wasan na kan hanyar su ta zuwa wasan mako na 11, a gasar Firimiya ta kasa NPFL.

Tawagar ta Adamawa United, za ta fafata da takwarar ta, ta MFM FC da ke jihar Legas.

Lamarin ya faru da karfe 11:45 na daren Jumu’a, inda ‘Yan fashin suka ‘kwace wayoyi, kudade da sauran kadarori na ‘yan wasan da mukarraban su, tare da yin awon gaba da direban motar.

Rahotannin baya-bayan nan, da suka fito daga majiyyoyi daban-daban a Benin, sun ce ‘yan fashin sun bukaci a biya su naira Miliyan 50 kudin fansa, kafin sakin Direban.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!