Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ana dakon abinda ka iya faruwa sakamakon cikar ritayar babban sefeton yan sandan kasar nan

Published

on

A yanzu haka ana dakon abin da ka iya kasancewa a cikin rundunar yan sanda ta kasa, sakamakon kammalar lokacin ritayar babban sefeto yan sandan kasar nan Ibrahin Idris a yau.

Ibrahim Idris wanda shine sifeton yan sandan kasar nan na goma 19, ya samu mukamin ne bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nadashi a ranar 21 ga watan maris din shekarar 2016 da ya karbi SolomArase.

Rahotanni sun bayyana cewar ya iso lokacin ritayar sa ne biyo bayan cika shekaru 35 yana aiki, sai dai wasu zantuka na kewayawa da ke rade-radin shugaban kasa Muhammadu Buharu zai kara masa wa’adi tun da dai bai cika shekara 60 a duniya ba.

Sai dai tuni al’umma suka fara sukar batun kara wa’din ga babban sifeton yan sandan, inda kuma suka ce suna dakon abin da zai faru kan batun babban sifeton nan da awannin 24

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!