Connect with us

Labarai

Ana  gudanar da bincike kan asusun NNPCL- Wale Edun

Published

on

Ministan Kudi da  Tattalin Arziki na Najeriya Wale Edun, ya tabbatar da cewa, ana  gudanar da bincike kan asusun kamfanin mai na NNPCL, domin inganta tsarin yadda kamfanin ke hada-hadar kudaden shigar sa.

Mninista Wale Edun, ya bayyana hakan ne a birnin Washington DC na Amurka,  yayin da ya ke jawabi a taron zuba jari a Nijeriya da aka gudanar a kasar ta Amurka.

A cewar sa  gwamnatin tarayya na kokarin daidaita  asusun ajiyarta.

Haka kuma, ya ce, kamfanin NNPCL na sa ran zai samar da karin kudaden shiga na musayar kudin waje ga asusun gwamnati.

Wale Edun, ya kuma yi karin haske da cewa, ana gudanar da binciken kwakwaf ne ga NNPCL domin fahimtar yadda kamfanin ya yi hada-hadar kudade a baya kafin cire tallafin man fetur da kuma bayan cire tallafin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!