Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

ASUU ba ta sanar da mu za ta shiga yajin aiki ba – Ministan Ilimi

Published

on

Gwamnatin tarayya ta yi zargin cewa ƙungiyar malaman jami’o’i ta ƙasa ASUU ba ta sanar da ita matakinta na tafiya yajin aiki ba.

Ministan Ilimi Adamu Adamu ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran ma’aikatar Bem Gboon ya fitar.

Sanarwar ta yi zargin cewa ma’aikatar ilimi ta ƙasa ta samu labarin tafiya yajin aikin wata guda na gargaɗi da ƙungiyar ASUU ta yi kamar yadda kowanne ɗan Najeriya ya samu labari.

Adamu Adamu ya kuma ce, ƙofofin ma’aikatar ilimi a buɗe suke domin tattaunawa da ƙungiyar, sai dai kuma babu wata sanarwa da ƙungiyar ta bata a hukumance.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!