Connect with us

Labarai

Atiku na daga cikin waɗanda suka haddasa mana rigingimu- PDP

Published

on

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP, ta yi iƙirarin cewa dan takararta na shugaban kasa a zaben da ya gabata na shekarar 2019 Atiku Abubakar na daga cikin waɗanda suka haddasa rigingimun da suka daɗe suna addabar jam’iyyar tare da cewa, ficewarsa ba za ta haifar da giɓi ba.

 

Mataimakin sakataren jam’iyyar kan harkokin yada labarai Ibrahim Abdullahi, ne ya bayyana hakan inda  ya yi iƙirarin cewa Atiku na ɗaya daga cikin waɗanda ke hadassa fitina a cikin jam’iyyar.

 

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ɗauki matakin ficewa daga PDPn ne a daidai lokacin da ya shiga wata haɗakar da ta haɗa jam’iyyun adawa a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar ADC, a wani abin da ya ambata da shirin tunkarar babban zaɓen 2027.

 

Tun farko Atiku Abubakar ya sanar cewa ya raba gari da jam’iyyar ta PDP inda ya ce ya yi hakan ne bisa la’akari da yadda ta sauka daga tsarin da aka kafa jam’iyyar.

 

Malam Abdallahi ya ce ficewar Atiku ta nuna ba zai iya samar da adalci ba ko da ya samu mulkin Najeriya duba ya abinda ya ayyana da rarraba kawunan jama’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!