Connect with us

Labarai

Ba mu kai samame gidan Obasanjo ba- EFCC

Published

on

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa, EFCC, ta musanta zargin da ake yi na cewa ta kai samame a   tsakiyar harabar Dakin Karatu na tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo da ke Abeokuta, a jihar Ogun tare da kama mutane 93 da ake zargi da damfara ta yanar gizo.

 

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Alhamis, mai magana da yawun hukumar, Dele Oyewale, ya ce wadanda aka kama suna cikin wani otal da ke makwabtaka da dakin karatun. Ya ce samamen ya biyo bayan sahihin bayanin leken asiri da ya nuna cewa wadanda ake zargin sun shirya gudanar da wani taro da ya saba da doka.

 

EFCC ta ce tana kan bakanta cewa matakin da ta dauka bai shafi dakin karatun kai tsaye ba, sai dai yana da nasaba da miyagun ayyuka da ke faruwa a kusa da wurin.

 

A baya dai, shugabannin Dakin Karatun sun bukaci EFCC da ta biya su diyya ta naira biliyan 3.5  

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!