Connect with us

Labarai

Ba mu sauya dokar haraji da majalisa ta sahale ba – Fadar Shugaban Najeriya

Published

on

 

Fadar shugaban kasa ta musanta zargin cewa ta sauya sabbin dokokin haraji a sirrance, bayan da ta ce babu wani gyara da ta yiwa dokokin wanda majalisar tarayya ba ta amince da shi ba.

 

Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da dan takarar shugaban kasa na jamiyyar LP a zaben da ya gabata, Peter Obi tare da wasu kungiyoyin fararen hulla suka bukaci a dakatar da aiwatar da dokokin.

 

Da ya ke zantawa da manema labarai, hadimin shugaban kasa kan kafafen yada labarai, Mr Temitope Ajayi ya ce babu wata sukar yan adawa da za ta hana aiwatar da dokokin a watan Junairu.

 

Ya ce har yanzu babu wata hukuma da ta fito fili ta yi zargin cewa an sauya dokoki, inda ya bayyana masu yada zarge-zargen a matsayin yan adawa dake kokarin haifar da ruɗani kan manufofin gwamnatin.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!