Connect with us

Labarai

Ba ni da niyyar barin Jam’iyyar NNPP- Sanata Kwankwaso

Published

on

Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaben da ya gabata na shekarar 2023 karkashin jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce ba shi da niyyar barin jam’iyyar, duk da cewa a shirye yake ya tattauna da sauran ‘yan siyasa kafin zaɓen 2027.

 

Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana hakan ne a taron kwamitin zartaswa na ƙasa da aka gudanar a Abuja, inda ya bayyana NNPP a matsayin “amaryar siyasar Najeriya” mai cike da manufofin ci gaba da kula da al’umma.

 

A nasa bangaren, sakataren jam’iyyar na ƙasa, Dipo Olayoku, ya ce NNPP na da shiri sosai domin tunkarar zaɓen gwamnan jihar Anambra wanda za a gudanar a watan  Nuwamba 2025 da kuma zaɓen kananan hukumomin Abuja a Fabrairu 2026.

 

Jam’iyyar ta kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi rijista da hukumar INEC domin samun katin zabe, tana mai jaddada cewa kujerar ku ita ce muryarku.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!