Connect with us

Labarai

Ba zan bari yan ta’adda su mamaye kowacce ƙaramar hukuma ba- Gwamna Zulum

Published

on

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa ba zai taɓa bari ‘yan ta’adda da masu tayar da ƙayar baya su mamaye kowace ƙaramar hukuma a jihar sa ba. 

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne bayan wata ganawa da suka yi da shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a fadar shugaban ƙasa da ke birnin tarayya Abuja, inda suka tattauna kan ƙalubalen tsaro. 

 

Yayin tattaunawar dai, Gwamna Zulum ya shaida wa shugaban ƙasa halin da yankin musamman ma  jihar Borno ke ciki dangane da matsalolin tsaro. 

 

Zulum da Shugaba Tinubu sun tattauna yadda gwamnatin tarayya da ta jihar za su haɗa kai domin shawo kan matsalar tsaro da ke addabar yankin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!