Connect with us

Labarai

Babban burinmu daga darajar Kano zuwa matsayin kasashen duniya- Kwamared Waiya

Published

on

‎Gwamnatin jihar Kano ta ce, babban burin ta, shi ne daga darajar jihar ya zuwa matsayin kasashen duniya irin su Turkiyya, England, Switzerland da Japan a fanin ayyukan raya kasa da samar da ababen more rayuwa ga al’umma.

‎Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ne ya bayyana hakan yayin da ya ke ganawa da ƙungiyar Abba Magajin Malam da Ƙungiyar Mawallafan Abba Gida-gida a ofishin sa.

‎Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya kuma jaddada muhimmancin manufar Kano First Agenda, ya na mai kira ga al’umma da su sanya ci gaban jihar a sahun farko a maimakon bambancin siyasa dake dakile cigaban al’umma.

 

A nasu jawaban, shugabannin ƙungiyoyin biyu, Alhaji Abubakar Sani da Alhaji Munnir Ibrahim, sun yaba wa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa goyon bayan da ya ke ba su, tare da gabatar da wasu buƙatu da za su taimaka musu wajen yaɗa ayyukan gwamnati.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!