Connect with us

Labarai

Sanata Barau ya kalubalanci gwamnatin Kano kan zarginsa da kalaman tunzura ‘yan ta’adda

Published

on

Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Barau I. Jibrin, ya shawarci gwamnatin Kano ta daina sanya siyasa a cikin batun tsaron jihar.

 

Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na Kano, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana cewa wasu kalamai da tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje da Sanata Barau suka yi a kwanan nan, suna da hatsarin iya kawo cikas ga kokarin tabbatar da tsaro da gwamnatin jiha da ta tarayya ke yi a yanzu.

 

Sai dai a cikin sanarwar da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Ismail Mudashir, ya fitar, Sanata Barau ya bayyana zargin gwamnatin jihar a matsayin maras tushe, yana mai kalubalantar gwamnatin ta fitar da bidiyon da ke nuna ya yi maganar da za ta iya ta’azzara matsalar tsaro.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!