Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Bruno Fernandes ya koma Manchester United

Published

on

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United dake kasar Ingila ta tabbatar da daukar dan wasa Bruno Fernandez daga kungiyar kwallon kafa ta Sporting Lisbon dake Kasar Portugal.

Bruno Farnandez ya sanya hannu kan kwantiragin shekaru biyar da rabi, akan Fam Miliyan hamsin da biyar, Inda yake da damar karawa idan har kwantiragin idan ya kare.

Bruno mai shekaru 25 a duniya, ya bugawa Kasar Portugal wasanni 137, inda ya zura kwallaye 63, sannan ya taimaka aka zura kwallaye 52.

Kuma yana cikin jerin yan wasan da suka lashe gasar UEFA Nations Cup League a 2019, wato kofin kasashen nahiyar turai.

Da yake jawabi, sabon dan wasan ya bayyana jin dadinsa a da kasancewa a kungiyar ta Manchester United, inda ya bayyana cewa, ya kasance masoyin Manchester United tun zamanin da Cristiano Ronaldo yake jan zarensa a kungiyar.

Ya kara da cewa zai yi iya kokarinsa wajen ganin Manchester ta samu nasarori da dama, musamman ma a kakar wasanni ta bana.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!