Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya ce nan ba da dadewaba za’a komawa makarantu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce da zarar an dage dokar hana zirga-zirga tsakanin jihohi a kasar nan zata fara shirye-shirye kan yadda za’a koma makarantu a kasar nan.

Karamin ministan Ilimi Emeka Nwajiuba ne ya bayyana hakan a yayin da kwamitin shugaban kasa kan yaki da cutar Corona ke gudanar da taron manema labarai da ya saba a kullum, yana mai cewa, gwamnatin tarayya na bin matakan da suka dace ne, don bude makarantu a kasar nan gudun kar a yi gaggawa, hakan kuma ya jefa rayuwar al’ummar kasar nan cikin hadari.

Emeka ya kuma kara da cewa, har yanzu gwamnatin tarayya bata tsayar da tartibib lokacin da za’a koma makarantu ba, a don haka jama’a su yi watsi da duk waani rahoton komawa makaranta da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani.

Idan dai za’a iya tunawa, tun a watan Maris din da ya gabata ne gwamnatin tarayya ta rufe dukannin makarantun kasar nan, sakamakon yadda cutar Covid-19 ke kara karuwa a kasar nan.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!