Connect with us

Labarai

Cibiyar NCTC da Burtaniya sun karfafa hadin kai don yaki da ta’addanci

Published

on

Cibiyar yaki da ta’addanci ta Najeriya NCTC karkashin jagorancin ofishin mai baiwa Shugaban Kasa shawara kan tsaro tare da hadin gwiwar kasar Burtaniya sun kara karfafa hadin kai domin kara inganta Shirin kawo Karshen rikice rikice da yaki da ta’addanci a kasar nan

 

Shugaban cibiyar ta NCTC na kasa Manjo Janar Adamu Laka, ne ya bayyana hakan yayin bude kwas din na musamman ga shugabannin tsaro, na  Gold da Silver Commanders tare da  nazarin bayanan sirri, a taron da ya gudana  a jiya litinin a Abuja

 

Manjo Janar Laka wanda Birgediya Janar Eromisele lawani ya wakilta ya ce horon wani muhimmin mataki  ne na karfafa shirin kasa  wajan fuskantar manyan hare hare da kuma rikice rikice cikin gida.

 

A nasa jawabin mai Kula da yaki da ta’addanci na Burtaniya a yankin Afirka, Lan Tyler ya ce shirin horon wata dama ce ta musamman da ke hada hukumomi Daban -Daban domin Gina sabbin shugabanin tsaro a kasar nan. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!