Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ciwon kunne ya janyo tsaiko a shari’ar Ɗan saruaniya

Published

on

Kotun majistret mai lamba 58 ƙarkashin mai Shari’a Aminu Gabari ta yi umarnin a tsare injiniya Mu’azu Magaji Ɗan Saruaniya a asibitin Ƴan sanda.

Tun da fari dai an gurfanar da Ɗan saruaniya ne bisa zargin ɓata suna inda aka yi zargin ya saki baki a kan gwamnan Ƙano Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

A zaman kotun na ranar Juma’a lauyan Ɗan Sarauniya ya yi suka a kan buƙatur masu gabatar da ƙara waɗanda suka roƙi a karantowa Ɗan Sarauniyar tuhumar da ake yi masa sakamakon baya ji sosai biyo bayan haɗari da yayi.

Yayin da yake ƙwarya-ƙwaryar hukunci mai shari’a Aminu Gabari ya ayyana cewar tabbas wanda yake da matsalar kunne ba za a karanta masa tuhuma ba tunda ba zai iya jin abin da aka karanta ba.

Sai dai kotun ta yi umarni a tsare shi a asibitin ƴan sanda zuwa ranar Litinin wanda ake sa ran ko kunnen na sa zai warke kamar yanda wakilin Freedom Radio Yusuf Nadabo Ismail ya ruwaito.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!