Labarai
COVID- 19 ‘Yan Najeriya mazauna kasashen ketare 288 ne suka dawo gida
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/08/ABIKE-DABIRI.png)
Hukumar kula da ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje ta sanar da cewa ‘yan Najeriya 288 ne suka dawo daga Hadaddiyar Daular Larabawa inda suka sauka a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe da ke Abuja yau.
Adadin da ya kawo mutane 2,641 kenan da aka kwaso daga Hadaddiyar Daular Larabawa tun bayan barkewar annobar cutar Covid-19.
Hukumar ta wallafa wannan sakon ne a shafinta na tiwita yau, inda ta ce za a yi wa mutanen gwajin kwayar cutar Corona, sannan kuma za a killace su har na tsawon makonni biyu kafin barinsu su tafi garuruwansu.
You must be logged in to post a comment Login