Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

COVID-19: ‘Yan wasa da jami’ai 36 sun kamu

Published

on

Kimanin ‘yan wasa da jami’ai talatin da shida ne a cikin kungiyoyi ashirin dake buga wasa a gasar firimiyar kasar Ingila suka kamu da cutar Korona a wannan watan na Janairu.

Hakan na kunshe ne ta cikin wata nasarawa da hukumar gudanar da gasar ta wallafa a shafinta na Internet.

Hukumar ta ce an samu mutane ashirin da bakwai da aka yiwa gwaji daga ranar hudu zuwa takwas ga watan Janairun bayan haka aka samu Karin mutane goma tsakanin ranar Juma’a zuwa Lahadi da suka gabata.

An dai gudanar da gwaji har zagaye biyu kan ‘yan wasan da kuma jami’an kimanin dubu biyu da dari biyar da casa’in da uku, yayin da sakamakon ya nuna mutane talatin da shida na dauke da cutar.

Sanarwar ta kuma ce, duk wanda ya kamu da cutar ta Korona zai killace kansa tsawon kwanaki goma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!