Connect with us

Labarai

Dakarun Operation Hadin Kai sun tarwatsa sansanin yan ta’adda a Sambisa

Published

on

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya na Operation Hadin Kai, sun kai wani hari ta sama inda suka tarwatsa wani sansanin ’yan ta’adda ne a dajin Sambisa a jihar Borno.

Wannan na cikin wata sanarwar da Daraktan hulɗa da jama’a na Rundunar Sojin Sama Air Commodore Ehimen Ejodame ya fitar.

Sanarwar ta bayyana cewa, aikin ya biyo bayan leƙen asiri da aka gudanar a yankin Kashomri da Sambisa, inda bayanan suka nuna motsin ’yan ta’adda a wasu gine-gine da suke amfani da su a matsayin maboya.

Ya ce, jiragen rundunar sun kai hare-hare ta sama kan wuraren da aka tabbatar suna da alaƙa da ayyukan ’yan ta’adda, bayan tattara sahihan bayanai daga jiragen leƙen asiri da bayanan sirri.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, dakarun za su ci gaba da ayyukan da suka shafi tabbatar da tsaro a yankunan da abun ya shafa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!