Connect with us

Labarai

Dakarun Soji na rundunar Operation MESA sun hallaka ƴan bindiga 19 a Kano

Published

on

Dakarun rundunar sojin Najeriya, sun samu nasarar murkushe wasu ƴan bindiga da kuma wani yunƙurin da suka yi na kai hari a wasu ƙauyuka na ƙaramar hukumar Shanono a jihar Kano.

Rundunar sojin sama ta Operation MESA, da ke ƙarƙashin birged na uku da ke Kano ne suka jagoranci aikin bayan samun bayanan sirri da suka ce sun samu kan yunƙurin ƴan bindigar na kai harin.

Wata sanarwa da jami’in yada labaran sashen, Babatunde Zubairu ya fitar, ta ruwaito cewa,  ƴan bindigar sun shiga  a ƙauyen Unguwan Tudu da Unguwar Tsamiya da Goron Dutse a ƙaramar hukumar Shanono da misalin ƙarfe biyar na yamma a ranar 1 ga watan Nuwamba.”

Sanarwar ta kara da cewa, an samu nasarar kashe ƴan bindiga 19 a gumurzun, sai dai  sojoji guda biyu, sun rasa rayukansu.

Kwamandan sashen Birgediya Janar Ahmed Tukur ya buƙaci mutanen yankin su ci gaba da gudanar da harkokinsu, sannan ya yi kira gare su da su riƙa sa ido kan abubuwan da ke wakana tare da kai musu bayani da gaggawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!