Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dalibi ya kashe kansa yayin da yake shekarar karshe a jami’a

Published

on

Hukumar gudanarwar jami’ar UNIBEN da ke jihar Edo ta tabbatar da mutuwar daya daga cikin daliban ta wanda ake zarkin ya kashe kansa ne a cikin daki.

An dai gano gawar dalibin ne mai suna Adams a cikin dakin sa da ke yankin Ekosodin a karamar hukumar Ovia ta arewa maso yamma a jihar ta Edo.

Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa dalibin na shekarar ta biyar ne a jami’ar inda ya ke karantar ilimin nazarin kwamfuta.

Wasu shaidun gani da ido sun shaidawa manema labarai cewa an yiwa Adams ganin karshe ne lokacin da ya mika aikin da aka bashi ga malamin sa kana ya koma wurin kwanan dalibai inda daga nan ke kuma ba’a kara jin duriyar sa ba.

Sai dai daga bisani aka gano gawarsa bayan da ‘yan uwansa suka ziyarce shi bayan da suka balla kofar dakin da ya ke ciki.

Sai dai a lokacin da hukumar makarantar ke tabbatar da faruwar al’amarin ita kuwa rundunar ‘yan sandan jihar bata ce komai ba kan mutuwar dalibin.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!