Connect with us

ilimi

Dalilan da suka sanya muka janye malamai – Ƙiru

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce rashin malamai a makarantun gwamnati shi ne dalilin da yasa ta janye malaman da ta tura makarantun sa kai da kuma makarantun al’umma wato community schools.

Kwamishinan ilimi na jihar Malam Muhammad Sanusi Sa’idu Ƙiru ne ya bayyana hakan jim kaɗan bayan kammala shirin Barka da Hantsi na nan Freedom Radio.

Malam Muhammad Sa’idu Ƙiru ya kuma ce sakamakon janye malaman da gwamnatin jihar kano ta yi da yawa daga cikin makarantun al’umma sun dawo ƙarƙashin gwamnati.

“Dama can doka ba ta bada damar gwamnati ta kai malamai makarantun sa kai ko na al’umma, shi ya sa daga baya muka ga dacewar dawo da su makarantun gwamnati don su ci gaba da bada gudunmawaa” in ji Ƙiru.

Kwamishinan ya kuma jajjada cewa har yanzu tsarin bada ilimi kyauta kuma dole yananan a jihar Kano domin samar da ilimi ga kowa da kowa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!