Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Dan takarar jihar Benue karkashin jam’iyyar APC yayi watsi da sakamakon gwamna

Published

on

Dan takarar gwamnan jihar Benue karkashin jam’iyyar APC mista Emmanuel Jime yayi watsi da sakamakon gwamnan da hukumar zaben ta sanar.

A jiya ne dai dan takarar jam’iyyar APC ya yi watsi da sakamakon da hukumar ta INEC ta fitar da ke ayyana gwamna Samual Ortum na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben.

Emanuel Jime ya shaidawa manema labarai cewar ko kadan bai amince da sakamakon ba kuma zai kalubalance shi a gaban kuliya.

A cewar say a zama wajibi ya garzaya kotu domin neman hakkin sa akan gwamna Otom wanda ya zarga da murde zaben da ya gudana.

Ya kuma yi zargin mafiya yawan kuri’un da ake cewa gwamnan ya samu, ya same su ne tas hanyar bankarawa da tursasawa masu zabe su zabi abin da bas hi suke so ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!