Connect with us

Labarai

Dangote ya shigar da karar shugaban Hukumar lura da albarkatun man fetur kan zargin al’mundahana

Published

on

Shugaban matatar man fetur ta Dangote,  Aliko Dangote, ya shigar da ƙorafi ga Hukumar ICPC mai yaki da cin hanci a Najeria yana zargin Shugaban Hukumar lura da albarkatun man fetur, Farouk Ahmed, da cin hanci da almundahanar kudade.

 

A ƙorafin da ya miƙa ta hannun lauyansa, Dangote ya buƙaci a kama, bincika tare da gurfanar da Farouk bisa zargin kashe fiye da dala miliyan bakwai wajen karatun ‘ya’yansa a Switzerland, ba tare da sahihin tushen kuɗi ba.

 

Jaridar Punch ta ruwaito Dangote ya ce Farouk ya yi amfani da mukaminsa wajen karkatar da kuɗaɗen gwamnati don amfanin kansa, lamarin da ke saɓa wa dokar rikon amana ga jami’an gwamnati.

Inda ya bukaci ICPC ta ɗauki mataki cikin gaggawa domin kare gaskiya da martabar gwamnati a kasar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!