Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Daya ga watan Nuwamba itace ranar matasa – Buhari

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da ranar 1 ga watan Nuwamban kowacce shekara a matsayin ranar Matasa.

Ministan wasanni Sunday Dare ne ya bayyana hakan ta shafin san a Twitter yana mai cewa shugaba Buhari ya amice da ranar ne a wajen taron majalisar zartaswa na kasa da aka saba gudanarwa a larabar kowanne mako.

Sunday Dare ya ce shugaba Buhari ya amince da ranar ne da nufin yin gangami da wayar da kan matasa, tare da lalubo hanyoyin ciyar sa su gaba da kuma gyara rayuwar su kasancewar su ne zasu jagoranci kasar nan a nan Gaba.

Taron majalisar zartaswar wanda aka gudanar ta kan Internet dai ya sami halartar mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osibanjo da sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha da sauran Ministoci.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!