Connect with us

Labarai

DSS na tauye mini hakki na samun adalci – Abubakar Malami

Published

on

Tsohon ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami (SAN), ya zargi hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da wasu ayyuka da ya ce suna da nufin tauye masa haƙƙinsa na samun adalci a shari’ar da ake yi masa.

A wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Mohammed Bello Doka ya sanya wa hannu, Malami ya ce ana ci gaba da hana shi ganawa da lauyoyinsa lamarin da ke kawo masa cikas wurin kare kansa daga zarge-zargen da ake yi masa

Ya bayyana abin da hukumar ta DSS ke yi a matsayin wani mataki na yi wa doka zagon ƙasa.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, kama shi da aka yi ya zo ne a daidai lokacin da ya ke buƙatar ya kare kansa a shari’arsa da hukumar EFCC gaban babbar kotun tarayya.

Malami ya ƙara jaddada aniyarsa na kare kansa a gaban kotu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!