Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Dalilin da ya sanya ake ci gaba da tsare Ibrahim Magu

Published

on

Bayan da aka yi zargin cewa mukaddashin hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC Ibrahim Magu na da lam’a a jikin sa, har kawo ranar Alhamis tswon kwanaki 4 kenan yana tsare.

Ana zargin cewa Magun ya aikata wasu manyan laifuka da suka hadar da sace kudaden da aka sato da sayar da kadarorin da aka kwato da kuma mayar da wasu jami’an hukumar ta EFCC shafaffu da mai wajen gudanar da ayyukan bincike da dai sauran su.

Kawo yanzu mukaddashin hukumar EFCC na fuskantar kwamitin bincike da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kafa kan zarge-zargen da ake masa.

Karin labarai:

Kwamitin fadar shugaban kasa ya gayyaci wasu manyan jami’an hukumar EFCC

Hukumar EFCC ta gano ma’aikatan bogi 1000 a jihar Kwara

Kwamitin wanda tsohon babban alkalin kotun daukaka kara mai shari’a Ayo Salami ke jagoranta ya yin da kuma akwai hukumomin tsaro da suka hada da ‘yan sanda da jami’an DSS a matsayin wakilan kwamitin.

Ministan shari’a kuma Atoni janaral ne ke zargin Magun da aikata wadancan laifuka.

Rahotanni sun bayyana cewar, tun a shekarar 2015 ne ake samun sabani tsakanin Magu da Abubakar Malami.

‘Yan Najeriya na zuba ido don ganin yadda zata kaya da zarge-zargen da ake yi wa Magun idan har sun tabbatar da su bayan da aka dakatar da shi daga kan mukamin sa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!