Connect with us

Labarai

DSS ta ceto sakataren karamar hukuma a Kano bayan sace shi

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da cewa jami’an sun yi nasarar ceto sakataren gudanarwa na karamar hukumar Kibiya, Alhaji Hamza Durya, bayan kwanaki da aka sace shi.

Rahotanni sun ce an sace shi ne a daren Juma’a a gidansa da ke kauyen Durya cikin karamar hukumar Kibiya, inda wasu mahara dauke da makamai, kimanin mutum shida, suka iso kan babura suka tafi da shi ba tare da sun harbe kowa ba.

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Ibrahim Waiya ya fitar, ya ce jami’an tsaro sun gudanar da aiki na hadin gwiwa wanda ya kai ga ceto mutumin tare da kama mutane biyu da ake zargi, inda aka ce sun samu raunukan harbi yayin aikin.

Gwamnatin ta yaba da kokarin jami’an tsaro, tana mai cewa hakan na nuna yadda dabarun tsaro ke aiki a fadin kananan hukumomi 44 na jihar, tare da jaddada kudirin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!