Labarai
DSS Ta gargadi ‘Yan Sanda kan yiwuwar sabon hari a Kwara da Neja

Hukumar Tsaron farin kaya ta DSS ta yi da gargadin tsaro ga rundunar ‘yan sandan jihar Kwara kan yiwuwar kai wani sabon hari a kauyen Gbabe da ke karamar hukumar Baruten.
Gargadin dai na zuwa ne kwanaki kadan bayan mummunan harin da aka kai a kauyen Woro da ke karamar hukumar Kaiama, inda aka kashe mutane da dama tare da tilasta wa wasu tserewa.
Hakan na cikin wata wasika mai dauke da sa hannun Daraktan DSS na jihar ta Kwara J.S. Adams, mai dauke da kwanan watan 5 ga Fabrairun 2026.
Sanarwar ta yi karin haske kan taruwar wasu gungun mutane dauke da makamai da ake zargin ‘yan kungiyar Mamuda ne a kusa da Kiyoru, gundumar Gwanara, da ta ce akwai yiwuwar su kai hari kan al’ummar Gbabe, tare da jaddada bukatar kara tsaurara matakan tsaro domin kauce wa tabarbarewar doka da oda.
Hukumar ta kuma tunatar da tarihin ayyukan ta’addanci da kungiyoyin makamai ke yi a yankin Kainji, tare da bukatar jami’an tsaro su dauki matakan kariya cikin gaggawa.
You must be logged in to post a comment Login