Kaduna
El-rufa’I ya kayyadewa masu adai-daita sahu wuraren zirga-zirga a Kaduna
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/07/Napep-Kaduna.jpeg)
Gwamnatin jihar Kaduna ta ce daga ranar litinin mai zuwa ne dokar da gwamnatin jihar ta sanya ta hana amfani da baburan adai-daita sahu bin wasu manyan hanyoyin jihar za ta fara aiki.
Shugaban hukumar kula da harkokin sufuri ta jihar Kaduna Malam Lawal Musa Usman ne ya bayyana hakan a zantawar sa da manema labarai.
“Dokar zata dakatar dasu su rika aiki a manyan hanyoyi kamar, Ali Akilu Road, Ahmadu Bello Way da kuma Western by Pass da wuraren Unguwar Rimi” a cewar sa.
Wakilin Freedom Radio Kaduna, Aliyu Abdullahi Jama’are ya rawaito Lawal Musa na cewa ce anyi hakan ne domin dakile yawaitar afkuwar hadura a manyan titunan jihar.
You must be logged in to post a comment Login