Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

El-rufa’I ya kayyadewa masu adai-daita sahu wuraren zirga-zirga a Kaduna

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce daga ranar litinin mai zuwa ne dokar da gwamnatin jihar ta sanya ta hana amfani da baburan adai-daita sahu bin wasu manyan hanyoyin jihar za ta fara aiki.

Shugaban hukumar kula da harkokin sufuri ta jihar Kaduna Malam Lawal Musa Usman ne ya bayyana hakan a zantawar sa da manema labarai.

“Dokar zata dakatar dasu su rika aiki a manyan hanyoyi kamar, Ali Akilu Road, Ahmadu Bello Way da kuma Western by Pass da wuraren Unguwar Rimi” a cewar sa.

Wakilin Freedom Radio Kaduna, Aliyu Abdullahi Jama’are ya rawaito Lawal Musa na cewa ce anyi hakan ne domin dakile yawaitar afkuwar hadura a manyan titunan jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!