Connect with us

Labarai

Fiye da mutum miliyan 8 ne suka yi rijistar zaɓe ta Internet- INEC

Published

on

Hukumar Zaɓe ta Najeriya INEC, ta bayyana cewa fiye da  ƴan Najeriya miliyan takwas ne suka kammala rajistar zaɓe a matakin farko ta intanet, yayin da ake ci gaba da gudanar da rajistar masu kaɗa ƙuri’a a faɗin ƙasa.

Hukumar ta INEC ta cikin wani rahoto da ta fitar a birnin tarayya Abuja, ta ce, baya ga waɗanda suka yi rajistar a matakin farko, akwai kuma mutane miliyan ɗaya da dubu bakwai da suka kammala cikakkiyar rajistar.

Bisa ga ƙididdigar mako na tara dai jihar Imo ce ta fi yawan masu rajista da mutane dubu takwas da dari biyu da sittin da shida da ɗari takwas da hamsin, wanda ke daidai da kashi 10.32 cikin dari. Sai Jihar Legas mai dubun shida da ɗari huɗu da sittin da ɗaya da dari shida da goma sha tara watau kimanin kashi 7.56 sai Jihar Yobe wadda ta fi ƙarancin masu rajista da mutum dubun biyu da ɗari bakwai da goma sha huɗu, watau kashi 0.03.

Haka kuma, an dakatar da rajistar a Jihar Anambra, bisa tanadin sashe na tara sakin layi na shida na Dokar Zaɓe ta shekarar 2022, har sai bayan zaɓen gwamna da za a gudanar ranar takwas ga watan Nuwamba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!