Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Ganduje : za mu farfado da kadadrorin gwamanti don samun kudin shiga

Published

on

Gwamantin jihar Kano ta jaddada aniyarta na ci gaba da farfado da tare da inganta kadarorin gwamnati da aka kyalesu ba a amfani dasu tsawon lokaci domin samun kudin shiga.

Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan yayin gabatar da taron majalisar zartarwa na mako-mako, inda ya karbi bakuncin kamfanoni guda biyu dake neman hadin gwiwa da gwamnatin domin inganta wasu kadarorinta.

A cewar sa, tuni aka samu kamfani na farko da ya gabatar da kudiri akan neman hadin gwiwa da gwamnatin Kano wajen mayar da kamfanin Triumph kasuwar ‘Yan canji.

Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya kuma godewa ma’aikatar ilimi mai zurfi da lafiya da muhalli bisa ga yadda suka jajirce wajen ganin yara sun koma makaranta.

Wakiliyar mu Zahrau Nasir ta ruwaito cewa, gwamna Ganduje kafin fara taron majalisar zartarwar a yau, sai da ya mika motar agajin gaggawa ga daraktan hukumar kashe gobara ta jihar Kano wadda Alhaji Aminu Dantata ya bada tallafi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!