Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Ganin kimar na gaba ne ya sa muka amince da sulhu game da rikicin da ya dabai-baye majalisa-Kabiru Alhassan Rurum

Published

on

Tsohon shugaban majalisar dokokin jihar Kano Kabiru Alhassan Rurum, ya ce, ganin kimar na gaba shi ya sa suka amince da sulhun da aka yi musu game da rikicin da ya dabai-baye majalisar dokokin a ‘yan kwanakin nan.

Kabiru Alhassan Rurum ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai da bangarensa ya gudanar a daren larabar da ta gabata.

Ya ce, tun da farko dama ba su nemi sauyin shugabancin don biyan bukatun kansu ba sai don neman gyara game da yadda ake jagorancin majalisar.

A nasa bangaren Abdullahi Chiromawa wanda shi kadai ne dan majalisa daga jam’iyyar PDP ya ce, duk da cewa ba jam’iyyar sa ce ta sa baki cikin lamarin ba amma ya yi biyayya ga matakin da shugabannin bangaren da yake goyon baya suka dauka na amincewa da sulhun.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!