Connect with us

Labarai

Gobara ta lalata dukiya ta miliyoyin kudi a Kasuwar Sokoto

Published

on

Wata gobara da ta tashi a tsohuwar kasuwar jihar Sokoto, da ake zargin ta samo asali sanadiyyar wutar lantarki, ta ƙone shaguna da dama. 

 

Rahotonni sun bayyana cewa, Gobarar ta lalata kaya da dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira.

 

Hukumar bada agajin gaggawa ta Najeriya NEMA shiyyar jihar ta ce, tawagarta ta kai daukin gaggawa ta garzaya wurin nan take bayan samun rahoton lamarin, tare da haɗin gwiwar Hukumar SEMA da Sashen Kashe Gobara.

 

NEMA ta kuma ce, haɗin gwiwar hukumomin ya taimaka wajen shawo kan gobarar tare da hana ta yaɗuwa zuwa sauran sassan kasuwar.

 

NEMA ta kara da cewa za ta ci gaba da fitar da ƙarin bayani game da lamarin yayin da ake samun sababbin bayanai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!