Connect with us

Labarai

Gombe: Ƴan sanda sun kama ƙasurgumin ɗan bindiga

Published

on

Rundunar ‘yan sandan Jihar Gombe ta kama wani mutum mai suna Adamu Adamu mai shekaru talatin da ake zargin cewa ɗan bindiga ne da ke aikata ta’ addanci a tsakanin kan iyakar Najeriya da Kamaru.

 

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar DSP Buhari Abdullahi, ne ya bayyana hakan ya na mai cewa an kama wanda ake zargin ne a ranar 4 ga watan nan da muke ciki na Oktoba.

 

Ya ce, an kama shi ne bayan samun bayanan sirri da suka nuna cewa ya na tare da wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane.

 

Ya kuma ce, a yayin samamen da CSP Ali Madaki ya jagoranta a ƙarƙashin rundunar Operation Hattara, ‘yan sanda sun gano boyayyen wurin makamai a kusa da kauyen Wuro Biriji a Jihar Adamawa.

 

Ya ƙara da cewa, An kwato bindigogi kirar AK 47 guda biyu da harsasai 80 sai sarkoki da wuka da makulli da kuma jakunkuna hudu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!