Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Good Friday: Gwamnatin tarayya ta ayyana Juma’a da Litinin a matsayin ranar hutu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun Juma’a 15 da Litinin 18 ga Afrilu, 2022, domin gudanar da bukukuwan good Friday da kuma Easter Monday na bana.

Wannan na cikin wata sanarwa da babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Dakta Shu’aib Belgore ya fitar a madadin ministan harkokin cikin gida Ogbeni Rauf Aregbesola.

Cikin sanarwar Aregbesola ya buƙaci Kiristoci da su yi koyi da halayen sadaukarwa, haɗin kai, gafara, alheri, soyayya, zaman lafiya da haƙuri, irin na Yesu Kiristi.

Don haka ya yi kira ga Kiristoci da sauran ƴan Najeriya da su yi amfani da bikin Easter na bana wajen yin addu’a domin kawo ƙarshen duk wani kalubalen tsaro da ke addabar kowane ɓangare na ƙasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!