Connect with us

Labarai

Gwamna Abba Kabir ya sauya sunan kwalejin wasanni zuwa sunayen yan wasa 22 da suka rasu

Published

on

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sauya sunan kwalejin horas da matasa harkokin wasanni zuwa sunayen tawagar ‘yan wasan Kano 22 da suka rasu a kan hanyarsu ta komawa gida daga gasar ƙasa a watan jiya na Mayu.

 

Yayin wani biki a gidan gwamnatin jihar, Gwamna Abba ya sanar cewa daga yanzu za a dinga kiran kwalejin Kano State Sports Institute da sunan Kano State 22 Athletes Sports Institute domin tunawa da su.

 

Kazalika, ita ma hukumar harkokin wasanni ta sauya suna zuwa Kano State 22 Athletes Sports Commission.

 

Gwamnan ya bayar da sanarwar ne lokacin da wata tawagar wakilai ta uwargidan shugaban ƙasa Remi Tinubu ta kai ziyarar jaje, inda ta bayar da gudummawar naira miliyan 110.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!